Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Tsohon Gwamnan Sokoto Attahiru Bafarawa ya zargi yan siyasa da hannu wajen kashe-kashen makiyaya

Published

on

Tsohon Gwamnan jihar Sokoto Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa ya bayyana cewa yan siyasa ne ke da hannu wajen kashe-kashen da ake samu a fadin kasar nan wadanda ake danganta su da Fulani Makiyaya.

A wata tattaunawa da manema labarai jim kadan bayan kammala taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP da ya gudana a jihar Sokoto, inda ya tabbatar da cewa kashe-kashen siyasa ce zalla.

Bafarawa ya kuma kara da cewa wasu yan siyasa marasa kishin kasa ne ke amfani da mutane wajen cimma burin su na siyasa ko da kuwa hakan ka iya salwantar da rayukan jama’a.

Alhaji Attahiru ya kuma shawarci shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya rika amfani da shawarwarin da yan Najeriya ke bashi, batare da la’akari da wanda ya bada shawarar ko jam’iyyar sa ba.

Ya kuma kara da cewa abin da yan Najeriya ke bukata shine ingantaccen shugaba ko da kuwa daga wace jam’iyya yake.

RAK

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!