Connect with us

Labarai

Rundunar Yan sandan Anambra ta cafke matasa 2 da ake zargi da satar mutane

Published

on

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Anambra ta kama wasu matasa biyu da ake zargi da aikata laifukan garkuwa da mutane da kuma  fashi da makami, a garin Umudioka da ke karamar hukumar Dunukofia.

 

Rundunar, ta cikin haka ne ta ikin wata sanarwa da mai magana da yawunta DSP Tochukwu Ikenga ya fitar.

 

Sanarwar ta ce, an samu nasarar kama matasan da ake zargi ne biyo bayan samun bayanai daga wata mata da ta kubuta bayan da suka yi garkuwa da ita a baya-bayan nan. 

 

Wadanda aka kama din sun hada da Onele Solomon wanda aka fi sani da Federal da Simeon Chidera wanda shi kuma aka fi sani da Chaplet, dukkansu ‘yan shekaru 23.

 

Haka kuma, Sanarwar ta kara da cewa da zarar an kammala bincike za a gaggauta mika wadanda ake zargi gaban kotu domin daukar mataki na gaba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!