Connect with us

Kaduna

Rundunar Yan sandan Jahar Kaduna ta gayyaci tsohon gwamna El-rufa’i

Published

on

Gov-Nasir-El-Rufai.

Rundunar ‘Yan sandan jahar Kaduna ta gayyaci tsohon Gwamnan jihar, Nasir El-Rufa’i da sauran jagororin jam’iyyar ADC kan zargin yunkurin tayar da zaune tsaye.

Hakan na kunshe ne a cikin wata wasika da ke dauke da kwanan watan hudu ga wannan watan nan, da sa hannun mataimakin kwamishinan yan sanda mai kula da sashen binciken manyan laifuka Uzairu Abdullahi.

Wasikar ta bayyana cewa,  ta na bincike a kan zargin hada baki da tunzura alummar gari, da tayar da hargitsi.

A makon da ya gabata ne aka yi musayar yawu tsakanin Gwamnatin jahar Kaduna, da tsohon Gwamnan kan wasu ’yan daba da suka kai wa taron jam’aiyyar ADC hari a jahar, sannan suka jikkata wasu mahalarta taron.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!