Connect with us

ilimi

Sace daliban Kebbi hari ne kai tsaye ga makomar Najeriya- Ministar Mata

Published

on

Ministar harkokin Mata Imaan Sulaiman Ibrahim, ta nemi a gaggauta sakin dalibai mata 25 na jihar Kebbi da aka sace, ta na mai bayyana lamarin a matsayin hari kai tsaye ga makomar Najeriya.

A cikin wata sanarwa da ta fitar, Ministar ta ce, sace daliban ba wai kawai cin zarafin iyayensu ba ne, har ma yana nuna irin barazanar da ‘yan ta’adda ke yi wa ilimi da zaman lafiya a fadin Najeriya.

Ministar ta yi kira ga hukumomin tsaro da su ƙara matsa kaimi wajen ceto yaran cikin koshin lafiya tare da tabbatar da cewa irin wannan ta’addanci bai sake faruwa ba a ko’ina.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!