Connect with us

Labarai

Sarkin Kano ya nada sabon Dagacin garin Ganduje

Published

on

Mai martaba sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sunusi II, ya nada Malam Jamilu Sani Umar a matsayin sabon dagacin garin Ganduje da ke karamar hukumar Dawakin Tofa da kuma dagacin garin burji a karamar hukumar doguwa Dakta Musa Garba Usman.

 

Wazirin Kano Alhaji Sa’ad Shehu Gidado, wanda ya yi magana a madadin Sarki, ya hori  Dagatan da su  mayar da hankali wajen kula da lafiyar al’ummar yankunan su da kuma sanya idanu kan bakin da suke shigowa yankunan su ba tare da izini ba.

 

A nasu jawaban daban-daban, dagatan sun gode wa Mai martaba sarkin bisa nadin nasu.

 

Haka kuma, Sakin ya karbi bakuncin daliban jami’ar gwamnatin tarayya da ke Dutse a jihar jigawa bisa jagorancin shugaban dalibai na  jami’ar Muhammad Muhammad Zakari.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!