Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Sarkin Katsina ya dakatar da hakimi sakamakon zargin sa da alaka da ‘yan bindiga

Published

on

Masarautar Katsina ta dakatar da hakimin Kankara Alhaji Yusuf Lawal, sakamakon zarginsa da hannu wajen taimakawa ‘yan bindiga a yankinsa.

Wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren masarautar Katsina Alhaji Mamman Iso a madadin Sarkin Katsina Alhaji Abdulmumin Usman, ta tabbatar da dakatarawar.

To sai dai sanarwar mai dauke da kwanan watan 30 ga watan Afrilun jiya ba ta yi cikakken bayanin irin rawar da ya taka wajen tallafawa ‘yan bindigar ba.

Sanarwar ta kara da cewa masarautar ta kafa kwamitin bincike don gano gaskiyar lamarin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!