Labarai
Sarki Muhammadu Sanusi II ya nada Sarkin Hausawan Turai
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2019/09/fadar-sarki-a-Turai.jpeg)
Sarki Muhammadu Sanusi II ya nada Sarkin Hausawan Turai
Sarkin Kano Muhammadu Sunusi na biyu ya nada Dakta Surajo Jankado Labbo a matsayin Sarkin Hausawa na kasashen Turai a wani taron bikin Hausawa da aka gudanar a birnin Paris a makon da ya gabata.
Wannan shine karo na farko da sarkin Kano ya gudanar da zama a kasar waje, tare da shirya masa zaman fada cike da kaloli irin na gargajiya, da Hausawa mazauna kasar waje suka hallara a fadar ta sa.
Jaridar Daily Nigeria dai ta rawaito cewar a yayin zaman ne dai aka zabi Dakta Labbo a matsayin sarkin Hausawan mazauna kasar Turai, daga cikin wadanda suka halarci fadar sarkin a birnin Paris dai, sun hadar da gwamna Palaiseau, Gregoire de Lasteyrie.
Sarkin Kano dai ya sauka ne a Turai bayan da ya hallarci taron majalisar dinkin duniya karo na 74 da aka gudanar a birnin New York.
Sarkin dai na fuskantar kalubale da dama a nan gida da gwamna Abdullahi Umar Ganduje, sai dai na samun girmamawa a idon duniya.