Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

SARS: Ganduje ya dakatar da Salihu Yakasai

Published

on

Gwamnan Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya dakatar da mai bashi shawara na musamman kan yaɗa labarai Salihu Tanko Yakasai daga muƙaminsa.

Kwamishinan yaɗa labaran Kano Malam Muhammad Garba ne ya sanar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar.

An dakatar da Salihu Yakasai saboda bayyana wasu kalaman suka game da gwamnatin shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a cewar sanarwar.

Kafin dakatarwar dai Salihu Yakasai ya soki manufofin gwamnatin tarayya a shafinsa na Twitter.

Salihu Yakasai ya soki shugaba Buhari da ƙin yin magana kan koken da ƴan Najeriya ke yi game da ƴan sandan SARS.

Ko a ranar 18 ga watan Afrilun da ya gabata, gwamna Ganduje ya sauke kwamishinan ayyuka na jihar Injiniya Mu’azu Magaji Ɗan Sarauniya sakamakon wasu rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Ɗan Sarauniya ya wallafa bayanai dake nuna suka ga shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa marigayi Malam Abba Kyari.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!