Connect with us

Labarai

SERAP ta bukaci Shugaba Tinubu ya binciki yadda gwamnoni ke kashe kuɗaɗen tsaro

Published

on

Kungiyar SERAP mai rajin kare haƙƙin ɗan Adam da tabbatar da adalci a shugabanci a ayyukan gwamnati, ta bukaci Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu da ya kafa kwamitin bincike domin tantance yadda gwamnonin jihohi ke kashe kuɗaɗen tsaro tun daga watan Mayu 2015 zuwa yanzu.

SERAP ta bayyana cewa akwai buƙatar gwamnati ta fito fili ta fayyace yadda ake batar da waɗannan kuɗaɗen da aka ware don sha’anin tsaro, tare da ɗaukar mataki kan duk wanda aka samu da hannu a aikata almundahana ko amfani da su ba bisa ka’ida ba.

Kungiyar ta yi gargadin cewa ɓoye gaskiyar yadda ake kashe makudan kuɗaɗen tsaro na iya haifar da gibin amincewa tsakanin al’umma da shugabanni, lamarin da ka iya jefa tsarin mulkin dimokuraɗiyya cikin hatsari.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!