Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kungiyar SERAP ta bukaci shugaba Buhari ya umarci ministan shari’a ya dauki matakin gaggawa kan shari’ar badakalar cin hancin wadanda suka sauka daga mulki

Published

on

Kungiyar da ke rajin tabbatar da adalci a cikin ayyukan gwamnati da yan majalisu SERAP ta bukaci shugaban Kasa Muhammadu Buhari da ya umarci ministan shari’a kuma attorney Janar Abubakar Malami ya fara daukar matakin gaggawa kan shari’ar badakalar cin hanci da rashawa da ya hadar da gwamnoni masu ci da kuma wadanda suka sauka.

Wannan na kunshe cikin wata wasika da kungiyar ta aikewa shugaban kasa Muhammadu Buhari mai dauke da kwanan watan 5 ga watan Oktoba da ke dauke da sa hannun mataimakin daraktan kungiyar Timothy Adewale.

Ta cikin wasikar kungiyar ta nuna damuwar ta kan yadda ake kawo tsaiko wajen yanke hukuncin kan gwamnonin da aka zarga da cin hanci da rashawa a kasar nan, inda ta ce hakan ba abin da zai haifar sai kara karfafa ayyukan cin hanci da rashawa.

SERAP ta kuma ce abin takaici ne a ce hukuncin wadannan mutane na yin tafiyar Hawainiya, musamman ma gwamnonin da aka zarga da cin hanci da rashawa da halasta kudaden haramun, amma kotuna na jan cikin wajen yanke hukunci duk da an kama su da laifi.

Kungiyar ta ce wasu da ga cikin shari’ar wadanda aka zarga da cin hanci da rashawar da suka hadar da gwamnoni masu ci da wadanda suka yi ritaya anfaro ne tun a shekarar 2007 amma har yanzu kotuna basu yanke hukuncin ba.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!