Connect with us

Labarai

SERAP ta maka CBN a kotu kan rashin bada bayanan kudaden da aka tura wa kananan hukumomi

Published

on

Kungiyar rajin tabbatar da adalci da daidato da  yaki da cin hanci da rashawa SERAP  ta yi karar babban bankin kasa CBN kan rashin bada  cikakkun bayanan kudaden da aka biya kai tsaye ga kananan hukumomi 774 na kasar nan, ciki har da kudaden da aka aike wa kowace karamar hukuma.

 

Mataimakin shugaban kungiyar ta SERAP, Kolawole Oluwadare, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa daya fitar a yau  Lahadi.

 

Ya ce karar kungiyar ta biyo bayan wani hukunci da kotun koli ta yanke a watan Yuli, inda ta ce dole ne a biya kason kudaden da aka ware daga asusun tarayya da CBN kai tsaye ga kananan hukumomin da aka yi zabe, kuma babu wani gwamna da ke da ikon rikewa, sarrafawa ko kuma yin amfani da kudaden da aka tanadar wa kananan hukumomin.

 

A cikin karar da ta shigar a ranar Juma’ar da ta gabata a babbar kotun tarayya da ke jihar Legas, SERAP na nemi kotun da ta umarci bankin na  CBN ya bayyana bayanan duk wasu kudaden da aka biya kananan hukumomin 774 ciki har da kudaden da aka aika wa kowace karamar hukuma tun bayan hukuncin kotun koli.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!