Connect with us

Labarai

Kotu ta dage Shari’ar Kananan Hukumomin Kano

Published

on

Babbar kotun tarayya mai lamba uku karkashin jagorancin mai shari’a Simon Amobeda, ta sanya ranar 26 ga watan gobe na Mayu domin ci gaba da shari’ar da wasu jagororin jam’iyyar APC suka shigar, ta nema hana babban Bankin kasa CBN, sakar wa kananan hukumomin jihar Kano 44 kudaden su kai tsaye.

A zaman kotun na yau Litinin,  kungiyar ma’aikatan kananan hukumomi da takwararta ta Malaman makarantu da kungiyar ma’aikatan lafiya ne suka bukaci shiga cikin shari’ar.

Tun da farko kotun ta yi hukuncin rushe shugabannin hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Kano KANSIEC, tare da hana su gudanar da zaben kananan hukumomi da aka yi a watan Oktoban bara. 

Amma ita kotun ta yi hukuncin cewar kada CBN din da kuma hukumar rabon albarkatun kasa su rike kudaden.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!