Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Shari’ar Zaɓe: Alƙalai sun zauna don fara gabatar da shari’a

Published

on

Kotun ɗaukaka ƙara da ke zamanta a Abuja ta shirya tsaf domin fara karanta hukuncin shari’ar gwamnan Kano da kuma bangaren jamiyyar APC.

Tun da fari dai gwamna Abba Kabir Yusuf shi ne ya shigar da ƙara, inda yake ƙalubalantar hukuncin kotun sauraran zabe wadda aka gudanar a kano.

Sai dai a yau ne kotun ta sanya domin yanke hukunci, wanda a halin yanzu kowane ɓangare ya halarci zaman.

A ɓangaren gwamnati mai ci ta NNPP kwamishinoni da dama sun halarci Kotun ciki har da sakataren gwamnati da shugaban jam’iyyar na Kano Hashim Dungurawa da na Abuja Dauda Yusuf.

Haka kuma a bangaren APC akwai ƙaramar ministar Abuja Dr. Mariya Bunkure da Rabiu Sulaiman Bichi da Aminu Dabo da sakataren jam’iyyar Zakari Sarina da Mutari Ishak da kakakin jamiyyar APC Ahmda Aruwa da kuma dumbin magoya bayansu.

A daidai wannan lokaci ana jiran shigowar Alƙalan da zasu gudanar da shari’ar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!