Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kotu ta sake tabbatar da Ɗanzago a matsayin shugaban jam’iyyar APC a Kano

Published

on

Wata babbar kotun tarayya a Abuja ta tabbatar da rushe zaɓen shugabannin jam’iyyar APC a jihar Kano da ɓangaren gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya gudanar.

Alkalin kotun Justis Hamza Mu’azu ya kuma tabbatar da zaɓen shugabancin jam’iyyar ɓangaren tsohon gwamna Sanata Ibrahim Shekarau a ranar Juma’a.

Idan za’a iya tunawa a ranar 30 ga watan Nuwamba, kotu tayi hukuncin cewa zaɓen da ɓangaren gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya gudanar haramtacce ne.

Tunda fari dai, ɓangaren Sanata Ibrahim Shekarau sun nemi kotun ta ayyana zaɓen da ɓangaren gwamna Ganduje da suka gudanar a matsayin haramtacce, inda ɓangaren gwamna Ganduje suka hanzarta garzaya kotu domin ɗaukaka ƙara.

Sai dai a hukuncin na ranar Juma’a, kotun ta kori karar ta su, ta kuma nemi su biya abokan sharia’ar ta su naira miliyan ɗaya saboda ɓata musu lokaci da suka yi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!