Connect with us

Labarai

Shettima ya dawo bayan kammala taron MDD karo na 80

Published

on

Mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima ya dawo gida Najeriya bayan kammala babban taron Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 80 da aka gudanar a birnin New York tare da kai wata ziyarar aiki a ƙasar Jamus, da ya sauka a babban birnin tarayya Abuja.

A yayin zaman na mako guda na hulɗar ƙasashen duniya, Shettima ya gabatar da jawabin ƙasa na Shugaba Bola Tinubu inda ya yi kira ga cikakkun sauye-sauye a Majalisar Ɗinkin Duniya.

Haka kuma Shettima, ya jagoranci kare ikon Afirka kan albarkatun ma’adananta da aka ƙiyasta darajarsu a dala biliyan 700 tare da ƙarfafa hulɗa ta dabarun cigaba da Birtaniya da Gidauniyar Gates, da sauran manyan masu ruwa da tsaki a duniya.

Mataimakin shugaban ƙasar ya kuma tabbatar wa al’ummar Najeriya mazauna ƙasashen ketare  cewa gwamnatin Tarayya  za ta ci gaba da ganawa da su a harkokin gudanarwarta.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!