Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Shirya taron zumunci zai wanzar da zaman lafiya a ƙasa – Ɗan kadan Kano

Published

on

Ɗan kadan Kano kuma Dan majen Gwandu Alhaji Bashir Ibrahim Muhammad ya buƙaci al’umma da su riƙi zumunci a matsayin abinda zai ƙara kyautata alaƙarsu da yan uwan su a duk inda suke.

Alhaji Bashir Ibrahim ya bayyana hakan a ranar Litinin, a wajen taron zuriyar Marigayi Moddibo Mahmud da kuma gabatar da littafin tarihin zuri’ar.

Ɗan kadan Kanon ya ce, kowacce zuri’a tana yin ƙarko ne a duk sanda ƴaƴan cikinta suka ɗauki matakan ingantata musamman ta hanyar shirya taruka.

“Muna sane da tarihin yadda kowacce zuriya ke fara da kaɗan, sai kuma ta bazu zuwa sassan duniya ta ci gaba da yaɗuwa ta hanyar hayayyafa”.

“Zuri’ar Moddibo ta zo Kano ne tun daga zamanin marigayi sarki Abdullahi Maje Karofi ga shi a yanzu zuriyar ta fara tattaro kanta ta hanyar bincike da tuntuɓa”.

Alhaji Bashir Ibrahim ya kuma ce, ta hanyar shirya taron dangi ne za a san yawan zuri’a kuma zumunci zai ƙara danko da kuma samun haɗin kani da zaman lafiya.

Taron ya samu halartar ɗaukacin ƴaƴa da jikoki daga sassa daban daban na ƙasar nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!