Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Shugaba Buhari ya bukaci gudunmuwar bankin musulunci don bunkasa rayuwa

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bukaci gudunmawar bankin raya kasashen musulmi (IDB) wajen bunkasa bangaren samar da abubuwan more rayuwa a kasar nan.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai Femi Adesina ya fitar..

A cewar Femi Adesina ta cikin sanarwar, shugaba Buhari, ya bayyana hakan ne lokacin da ya ke ganawa da mataimakin shugaban bankin raya kasashen musulmi Dr. Mansur Mukhtar, a gefen taron kungiyar kasashen Afurka (AU) da ke gudana a birnin Yamai babban birniN Jamhuriyar Nijar.

Shugaba Buhari ta cikin snaarwar dai, ya kuma ce, yayin da adadin al’ummar kasar nan ke karuwa ba kakkautawa, akwai bukatar kara adadin kudaden da ake kashewa wajen samar da abubuwan more rayuwa.

Sanarwar ta kuma ruwaito, mataimakin shugaban bankin raya kasashen musulmi na duniya Dr. Mansur Mukhtar, na cewa, bankin zai ci gaba da bada gudunmawa wajen samar da abubuwan more rayuwa ga al’ummar Najeriya.

Yayin da a bangare guda, ya ce, nan ba da dadewa ba, shugaban bankin raya kasashen musulmin zai kawo ziyara  Najeriya domin bude reshen ofishin bankin a kasar nan.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!