Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Shugaba Buhari ya bukaci kasashen da aka ajiye kudin sata da su gaggaua dawo da su

Published

on

Shugban kasa Muhammadu Buhari ya bukaci kasashen da ake sace kudi a kai ajiya wajensu su gaggauta sakin kudaden ga kasashen da aka sato daga cikinsu cikin gaggawa ba tare da wani bata lokaci ba.

Shugaban kasar na fadin hakan yayin gabatar da jawabi a taron kasashen Afirka na bana a birnin Nouakchott da ke kasar Mauritania, wanda aka yi wa taken samun nasara kan yaki da cin hanci da rashawa, hanya daya da nahiyar Afirka da ta samu ci gaba mai dorewa.

Gabanin fara muhara kan yadda za a lalubo hanyar magance matsalar cin hanci da rashawa a Afirka, saida shugaba Muhammadu Buhari ya yi jawabin irin matakan da yake dauka domin kawar da matsalar a Najeriya.

Muhammadu Buhari ya ce nan gaba kadan zai shirya taron matasan Afirka a birnin tarayya Abuja, tare da hadin gwiwar shugaban kungiyar hadin kan Afirka AU Paul Kagame, wanda kuma shi ne shugaban Rwanda, domin tattauna yadda wakilcin Afirka zai kasance yayin babban taron Majalisar dinkin Duniya mai zuwa.

Har ila yau ya bayyana cewa babban taron da aka gudanar a kasar nan cikin watan Afrilun da ya gabata kan al’amuran tsaro da zaman lafiya, ya nuna karara irin illar da cin hanci da rashawa ke yi wa Afirka, a don haka ya bukaci hadin sauran shugabannin Afirka don ganin an magance matsalar.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!