Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu ya amince da biyan bashin wutar lantarki na Naira Tiriliyan 3.3

Published

on

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya amince da wani shiri na biyan bashin wutar lantarki da ya kai naira tiriliyan 3.3, domin gyara matsalolin da suka dade suna addabar bangaren wutar lantarki a ƙasar.

ta cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga ya fitar, gwamnatin ta ce bashin ya samo asali ne tun daga shekarar 2015 zuwa 2025, kuma an cimma matsaya cewa za a biya shi gaba ɗaya.

Tuni dai aka fara aiwatar da shirin, inda kamfanonin samar da wuta 15 suka rattaba hannu kan yarjejeniyar karɓar kusan naira tiriliyan 2.3, yayin da gwamnati ta ware sama da naira biliyan 500 domin fara biyan bashin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!