Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu ya gana da Gwamnan Kaduna Uba Sani

Published

on

Gwamnan Jihar Kaduna Sanata Uba Sani ya gana da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a Fadarsa da ke Abuja a ranar Juma’a, inda suka tattauna batutuwan tsaro, manyan ayyukan more rayuwa, da muhimman tsare-tsaren ci gaban Jihar Kaduna.

 

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar bayan ganawar.

 

A cewar sanarwar, gwamnan ya sanar da Shugaban Ƙasa dawowar masu ibada da aka sace daga coci-coci a garin Kurmin Wali da ke Karamar Hukumar Kajuru.

 

Gwamnan ya ƙara da cewa ganawar ta kuma tattauna kan fara aikin hanyar Birnin Gwari, da kuma muhimmancin gyaran hanyoyin Kaduna Eastern Bypass, Jere zuwa Kwoi zuwa Kafanchan, da Zaria zuwa Pambegua zuwa Saminaka, a matsayin muhimman hanyoyin zirga-zirga da ci gaban tattalin arziki.

 

Uba Sani ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da aiki tare da Gwamnatin Tarayya wajen inganta tsaro da bunƙasa manyan ayyukan more rayuwa a faɗin Jihar Kaduna.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!