Labarai
Shugaba Tinubu ya jajanta wa ƴan kasuwar Singa bisa iftila’in Gobara

Shugaban kasa Bola Tinubu ya jajanta wa ƴan kasuwar da suka tafka asarar miliyoyin naira da dukiyoyi bayan tashin gobara a Kasuwar Singa da ke jihar Kano.
Gobarar ta tashi ne da yammacin Asabar amma har safiyar Lahadi wuta na ci, lamarin da ya janyo mummunan asara a kasuwar.
Shugaba Tinubu – wanda ya nemi Gwamna Abba ya tattara bayanai kan gobarar – ya bayyana lamarin tamkar mummunan bala’i.
Haka kuma shugaban ƙasar ya nuna damuwarsa musamman kasancewar a mako biyu da suka gabata ma an samu gobara a kasuwar da ta lalata gomman shaguna da dukiyoyi.
Don haka ne ya nemi a gudanar da cikakken bincike kan dalilan de ke haifar da gobara a kasuwanni, lamarin da ke jefa ƴan kasuwa cikin mummunar asara da damuwa.
You must be logged in to post a comment Login