Labarai
Shugaba Tinubu ya musanta zargin da ake masa na ƙoƙarin mayar da Najeriya tsarin jam’iyya ɗaya

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya musanta zargin cewa gwamnatin sa na ƙoƙarin mayar da kasar nan a tsarin jam’iyya ɗaya ko raunana jam’iyyun adawa.
Shugaba Tinubu, ya musanta haka ne yayin da ya ke jawabi a wani taron shan ruwa a fadar shugaban Ƙasa da ke birnin tarayya Abuja.
Ya ce, kalubalen tsaro kamar ta’addanci da fashi da makami na bukatar haɗin kan kasa maimakon rabuwar kan siyasa.
Shugaban ya kuma bukaci al’ummar Najeriya da su bi tafarkin dimokuraɗiyya da magabata suka shimfiɗa, ya na mai cewa babu laifi idan wasu ‘yan siyasa sun sauya sheƙa, amma hakan ba ya nufin mayar da siyasar Najeriay kan tafarkin jam’iyya guda ɗaya ba ne.
You must be logged in to post a comment Login