Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu ya rantsar da kwamitin aikin Kidaya

Published

on

Shugaban kasa Bola Tinubu, ya rantsar da kwamatin da zai tsara yadda za a gudanar da kidayar jama’a.

Shugaban, wanda shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila, ya wakilta ya bai wa ‘yan kwamatin wa’adin mako uku da su gabatar da rahotonsu.

Wata sanarwa da mai magana da yawun fadar shugaban kasa, Bayo Onanuga, ya fitar ta ce Tinubu ya alakanta kidayar da abinda ke kawo ci gaban kasa.

Rahotonni sun bayyana cewa, Karo na karshe da Najeriya ta yi kidaya shi ne a shekarar 2006, inda kididdigar ta nuna cewa akwai mutane 140,431,790, yan asalin Najeriya da suka kunshi maza 71,345,488 da kuma mata 69,086,302.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!