Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu ya sauka a birnin Rome

Published

on

Shugaban ƙasa Bola Tinubu, ya isa birnin Rome na ƙasar Italiya domin halartar taron shugabanni na Aqaba Process, wanda zai tattauna kan batutuwan tsaro a yankin Yammacin Afirka.

 

Taron wanda aka assasa tun a shekarar 2015 na Sarki Abdullah II na Jordan tare da haɗin gwiwar Italiya, zai mayar da hankali kan yaduwar ta’addanci a yankin Sahel, laifukan da ke da alaka da ruwa a gabar tekun Guinea, da kuma tsattsauran ra’ayi ta kafafen intanet.

 

Tinubu zai yi ganawa ta musamman da wasu shugabanni don samar da hanyoyin magance matsalolin tsaro a nahiyar Afrika.

 

Yayin tafiyar tasa Shugaba Tinubu ya samu rakiyar manyan jami’an gwamnati ciki har da Ministan Harkokin Waje Bianca Odumegwu–Ojukwu, Ministan Tsaro Mohammed Badaru, da Mai ba da shawara kan tsaro Nuhu Ribadu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!