Connect with us

Labarai

Shugaban Ƴan kasuwar Kwari ya musanta sayar da ofishin yan kwana-kwana

Published

on

Shugaban gammayar ƙungiyoyin ƴan kasuwar Kantin Kwari Musa Umar Sanda Arzai, ya ce maganar cefanar da ofishin jami’an kashe gobara na kasuwar ba gaskiya bane biyo bayan zargin da yan kasuwar suka yi dake cewa, an sayar da ofishin har ma an fara gine shi.

Musa Umar Sanda Arzai ya bayyana hakan ne yayi zantawa da manema labarai a kasuwar ta kantin kwari.
Ya kuma kara da cewa hakan biyo bayan korafe-korafen da suka yita samu kan ana yin abubuwan da basu dace ba a wajen yasa hukumar kasuwar da ammincewarsu daukar wannan matakin.

Haka kuma ya bayyana cewa, sun karbi koken yan kasuwar kan harajin da suka ce an tsawwala musu, inda ya ce za su bibiyi batun tare da ɗaukar matakan da suka dace.

Shugaban ya kuma bukaci yan kasuwar da su kwantar da hankulansu domin kuwa, kungiya za ta yi duk abinda ya dace domin daidaita komai a kasuwar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!