Connect with us

Labarai

Shugaban Bola Tinubu ya gana da Gwamnonin jam’iyyar APC

Published

on

Shugaban  kasa Bola Ahmed Tinubu, ya yi wata ganawar sirri da Gwamnonin jam’iyyar APC mai mulki a fadar shugaban kasa da ke Abuja a daren ranar Laraba.

 

An gudanar da wannan ganawa ne sa’o’i kadan kafin babban taron Kwamitin Zartarwa na kasa na jam’iyyar wato NEC wanda za a yi a yau Alhamis.

 

Rahotonni sun bayyana cewa Gwamna Hope Uzodimma na jihar Imo, wanda ke jagorantar kungiyar Gwamnonin APC, ya jagoranci sauran gwamnoni zuwa fadar shugaban kasa, bayan sun kammala wata ganawa da suka yi a gidan gwamnatin jihar Imo da ke Asokoro a birnin tarayya Abuja.

 

jaridar Dialy Trust ta ruwaito cewa, ana sa ran ganawar za ta taimaka wajen cimma matsaya kan muhimman batutuwa kafin taron babban taron na jam’iyyar APC musamman batun mukamin Shugabancin  Jam’iyyar  na kasa, wanda ke ci gaba da haifar da ce-ce-ku-ce tun bayan saukar tsohon shugaban jam’iyyar, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, wanda ya yi murabus daga shugabancin APC a baya bayan nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!