Connect with us

Labarai

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya cire sunayen wasu daga cikin mutanen da ya yi wa afuwa.

Published

on

 

 

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya rattaba hannu kan takardun afuwar da ya yi ga wasu da aka yanke wa hukunci.

Bayan shawara da majalisar koli da ra’ayoyin jama’a, shugaban kasa ya sake duba jerin wadanda za a yi wa afuwa, inda ya cire wadanda suka aikata manyan laifuka kamar garkuwa da mutane, fataucin miyagun kwayoyi, da zamba.

 

Shugaban kasar ya ce matakin ya zama dole domin kare tsaro da kuma kula da hakkokin wadanda abin ya shafa. Ya kuma bada umarnin cewa nan gaba ofishin kwamiti mai ba da shawara kan afuwa zai koma karkashin ma’aikatar shari’a maimakon ma’aikatar ayyuka na musamman.

Haka kuma, ya umurci Attorney General na kasa da ya fitar da sabbin ka’idoji domin tabbatar da cewa duk wanda zai amfana da afuwa ya cika ka’idojin doka.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!