Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Masu laifi da ke buƙatar yafiya sun kai 320 a ƙasar nan – Abubakar Malami

Published

on

Ministan shari’a kuma antoni janar na ƙasa Abubakar Malami ya ce, ma’aikatar shari’a ta karbi buƙatu 320 a madadin wasu da aka yanke wa hukuncin kisa da ke bukatar neman afuwar shugaban kasa.

Malami ya yi wannan bayani ne a lokacin a taron kwamitin ba da shawara na shugaban kasa kan hakkin bada afuwa ga masu laifi.

A cewar Malami, tun lokacin da kwamitin ya gabatar da rahotonsa kuma ya ci gaba da hutu, ma’aikatar ta samu takardun buƙatu masu yawa na neman yafiya daga wajen shugaban kasa.

Malami ya kuma ce, ya zama wajibi kwamitin ya dawo bakin aiki, la’akari da yadda bukatar neman yafiya a wajen shugaban kasa yayi yawa daga wadanda aka yanke wa hukuncin kisa a kasar nan.

Ministan ya tabbatar da cewa kwamitin zai duba buƙatu guda 320 da ofishinsa ya karba zuwa yanzu kuma zai ba da shawara kamar yadda ya dace dangane da yin yafiyar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!