Connect with us

Labarai

Shugabancin Tinubu na tafiya bisa adalci wajen yin ayyukan raya ƙasa- Mohammed Idris

Published

on

Gwamnatin Tarayya ta ce, shugabancin Bola Ahmed Tinubu ya na tafiya bisa adalci wajen rarraba ayyukan raya ƙasa a dukkan yankunan Najeriya.

 

Ministan yaɗa Labarai Mohammed Idris, ne ya bayyana hakan ya na mai cewa manyan ayyuka kamar titin Lagos zuwa Calabar da na Sokoto zuwa Badagry da gadar Second Niger Bridge da kuma layin dogo a Kano sai Kaduna da Lagos, sun tabbatar da cewa babu wani yanki da aka nuna wa wariya.

 

Rahotanni sun nuna cewa, yankin Arewa maso Yamma ne ya fi cin gajiyar ayyukan da sama da naira tiriliyan biyar, amma sauran yankuna su ma sun samu muhimman ayyuka.

 

Haka kuma ya kara da cewa, gwamnatin ta jaddada cewa, shirin Renewed Hope Agenda zai tabbatar da cewa babu wani yanki da za a bari a baya wajen ci gaban ƙasar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!