Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Shugabar gidan talabijin na ARTV ta lashe zaben BON

Published

on

An zabi Shugabar gidan talabijin na ARTV dake Kano Hajiya sa’a Ibrahim a matsayin shugabar kungiyar kafafan yada labarai ta kasa .

 

Jaridar Kano Focus ta rawaito cewar Hajiya Sa’a Ibrahim ta kasance shugabar kungiyar a wani taro da aka gudanar na kungiyar karo na 72 , biyo bayan rashin cancanta da abokin hammayarta Yusuf Nadabo dan jihar Adamawa yayi.

 

Hajiya sa’a Ibrahim dai ita ce mataimakiyar shugabar kungiyar , kafin a zabe ta a matsayin shugabar kungiyar a yanzu.

 

Da take jawabi Hajiya Sa’a Ibrahim ta sha alwashin damawa da dukkanin mambobin kungiyar a kokarin tabbatar da cigaban kungiyar.

 

Ta kuma bayyana jin dadinta ga yadda zaben ya tafi ba tare da tashin hankali ba .

 

Zaman da kungiyar kafafan yada labarai za ta yi nna gaba za ta yi shine a Jihar Kano. An kafa kungiyar ne a 1973 a matsayin hadin gwiwar kafafan yada labarai masu zama kansu da na gwamnati.

 

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!