Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Siyasar Kano: Dauda lawan ya ajiye muƙaminsa don takarar ɗan majalisa

Published

on

Babban mai taimakawa Gwamnan Kano kan ci gaban al’uma Ahmad Dauda Lawan ya ajiye muƙaminsa domin tsayawa takara a zaɓen 2023.

A wata sanarwa da ya fitar, Ahmad Dauda ya ce, ya sauka daga muƙamin ne domin biyayya ga sabuwar dokar zaɓe.

Dauda Lawan ya ce, yana neman ɗan majalisar jihar mai wakiltar ƙaramar hukumar Tarauni.

Wannan dai na zuwa ne kwana guda bayan da Gwamna Ganduje ya bai wa masu riƙe da muƙaman siyasa da ke sha’awar takara umarnin ajiye aiki domin biyayya ga dokar zaɓe.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!