Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Siyasar Kano: Mahangar masana kan zaben kananan hukumomi

Published

on

Masana sun fara sharhi kan shirin hukumar zaɓe ta jihar Kano na gudanar da zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi a watan Janairun baɗi.

Dr. Sa’id Ahmad Dukawa na jami’ar Bayero ya shaida wa wakilinmu Bashir Sharfadi cewa, shirin zaɓen a kan lokaci abu ne da ya dace domin zai kawar da tsarin naɗa kantomomi.

Sai dai, ya ce akwai wasu abubuwa uku game da zaɓen da suka kunshi shiri kafin zabe da yayin zaben da kuma bayan zaben.

Dr. Dukawa yace yin adalci a yayin yakin neman zabe da kuma tabbatar da cewa an samarwa da hukumar zabe kayayyakin da take bukata, sai kuma yin adalci a yayin sanar da jam’iyyar da ta lashe zabe, shine abinda ke inganta kowanne irin zabe.

Hukumar zaɓen Kano dai ta yi alƙawarin yin duk mai yiwuwa wajen ganin tayi karɓaɓɓen zaɓe bisa adalci.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!