Connect with us

Labarai

Sojoji sun kama jagoran yan bindiga da ake zargi da addabar matafiya a hanyar Benue zuwa Taraba

Published

on

Rundunar Sojin Najeriya, ta sanar da cewa, dakarunta sun kama wani fitaccen jagoran ’yan bindiga da ake zargin ya daɗe ya na addabar matafiya a kan hanyar Benue zuwa Taraba.

Daraktan hulɗa da jama’a na rundunar sojin, Laftanar Umar Muhammad, ya bayyana a Jalingo cewa wanda aka kama Fidelis Gayama na cikin jerin mutanen da hukumomin tsaro ke nema a jihohin Benue da Taraba.

Ya kuma bayyana cewa, an samu nasarar kama shi ne a ƙauyen Vaase da ke ƙaramar hukumar Ukum ta jihar Benue, bayan samun sahihan bayanan sirri.

Ya ce binciken farko ya nuna cewa Gayama na da alaƙa ta kusa da wani fitaccen shugaban ƙungiyar ’yan ta’adda da ake nema, Aka Dogo.

Laftanar Umar Muhammad ya ƙara da cewa ana zargin Fidelis Gayama ne jagoran wata ƙungiyar masu aikata laifuka da ke kai hare-hare kan matafiya da al’ummomi a kan hanyar Kente–Wukari da kuma yankunan iyakar Benue da Taraba.

A cewarsa, wanda aka kama yana hannun sojoji a halin yanzu, kuma za a miƙa shi ga hukumomin da suka dace domin ci gaba da bincike da gurfanar da shi a gaban kotu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!