Labarai
Sojoji sun kashe kwamandan ‘yan ta’addan ISWAP

Dakarun rundunar hadin gwiwa ta Operation Haɗin Kai da ke aiki a yankin arewa maso gabshin Najeriya, sun sanar da nasarar kai wasu munanan hare-hare kan ƙungiyoyin ƴan bindiga da ke addabar yankin.
A cikin wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na rundunar, Laftanar Kanar Sani Uba ya fitar, ya ce bayanan sirri sun tabbatar da kashe wani babban kwamandan ƙungiyar ISWAP mai suna Julaibib a yankin Gujba.
A cewarsa, an yi nasarar kashe shugaban mayaƙan na ISWAP ne bayan wani artabu da aka yi tsakanin mayaƙan da dakarun soji a kusa da garin Kimba da ke ƙaramar hukumar Damboa ta jihar Borno, a ranar 30 ga watan Janairu.
“Wannan ci gaba mai mahimmanci ya kasance babban illa ga tsarin ƙungiyar ISWAP a yankin,” in ji sanarwar.
You must be logged in to post a comment Login