Connect with us

Labarai

Sojoji sun kubutar da fasinjoji sama da 20 da aka yi yunkurin garkuwa da su

Published

on

Rundunar Sojojin kasar nan sun dakile yunƙurin garkuwa da wasu fasinjoji a kan hanyar Otukpo zuwa Enugu a Jihar Benue, inda suka ceto fasinjojin su 24 daga motocin haya biyu da ke tafiya daga Jos zuwa Ibadan.

 

Ta cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ta ruwaito bayan samun kiran gaggawa, sojoji sun kai ɗauki bayan da suka yi musayar wuta da ’yan bindigar da suka tsere zuwa daji.

 

Kwamandan rundunar, Major General Moses Gara, ya yaba wa sojojin bisa gaggawar martani, tare da tabbatar da ci gaba da kare rayuka da dukiyoyi al’ummar yankin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!