Connect with us

Labarai

Sokoto: Mutane 7 sun rasu sakamakon fashewar Bam

Published

on

Akalla mutane  bakwai ne suka  rasu bayan wani Bam, ya tarwatse a ƙauyen Gwabro da ke Ƙaramar Hukumar Tangaza a Jihar Sakkwato.

Lamarin dai ya faru ne da yammacin jiya Litinin, a lokacin da waɗanda abin ya rutsa da su ke dawowa daga yawon Sallah a kan babura.

Rahotanni sun nuna cewa an dasa bama-baman ne a ƙarƙashin wata itaciya da sojoji ke amfani da ita a matsayin wajen hutu yayin sintiri.

Bayan fashewar, mutum shida sun mutu nan take, yayin da ɗaya daga cikin yara biyu da suka jikkata ta rasu washegari.

Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukumar Tangaza, Alhaji Ghazzali Rakah, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa waɗanda suka mutu mazauna ƙauyen Zurmuku ne, wanda ke maƙwabtaka da inda lamarin ya faru.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!