Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Susa da manjagara: Ganduje ya tsige Ɗansarauniya daga muƙaminsa

Published

on

Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ya sauke Injiniya Mu’azu Magaji Ɗansarauniya daga shugabancin kwamitin aikin janyo bututun iskar gas zuwa Kano, wanda aka yi wa lakabi da NNPC/AKK.

Jaridar Daily Nigerian ta rawaito Kwamishinan yada labarai Muhammad Garba ne ya sanar da tsige Mu’azu Magajin a daren jiya Litinin.

Gwamnati ta ce, ta sallame shi ne saboda gazawarsa a aikin da kuma rashin biyayya.

Gwamnan ya umarci shi da ya bada ragamar kwamitin ga mataimakinsa Aminu Babba Dan’Agundi

A watan Afrilun bara ne Gwamna Ganduje ya sauke shi daga muƙamin Kwamishina saboda yin murnar rasuwar shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa wato Abba Kyari a Facebook.

Daga bisani kuma Gwamnan ya ba shi shugabancin wannan kwamiti.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!