Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Tarihi: ko kun san me yasa Ja’afar Ja’afar ya yi gudun hijra

Published

on

A ranar 25 ga watan Okotaban 2018 babban editan jaridar Daily Nigerian da ake wallafawa a Internet Ja’afar Ja’afar ya bayyana gaban majalisar dokokin jihar Kano.

Ja’afar Ja’afar ya bayyana gaban majalisar ne don bada ba’asi kan binciken da majalisar ke gudanarwa ga me da zargin da ake yiwa gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje.

Zargin dai shi ne batun karɓar miliyoyin daloli a matsayin na-goro daga hannun ƴan kwangila.

Sai dai tun bayan hakan ne, Ja’afar Ja’afar ya yi gudun hijra zuwa ƙasar Burtaniya sakamakon zargin da yake na ana farautar rayuwar sa.

Ya ce, tun bayan da ya saki faifan bidiyon dala ya fara fuskantar barazana a rayuwar sa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!