Connect with us

Labarai

Tinubu ya tafi zuwa Turai domin kammala hutun shekara

Published

on

Shugaban Najeriya Bola Ahmad Tinubu ya bar Legas a yau Lahadi zuwa Turai don cigaba da hutunsa na karshen shekara.

ta cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban shawara kan harkokin yaɗa labarai Bayo Onanuga ya fitar, ya bayyana cewa shugaban zai kuma kai ziyara a hukumance zuwa Abu Dhabi, babban birnin Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa.

Shugaban ƙasar ta Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ne ya gayyaci Tinubu domin halartar wani taro na mako ɗaya kan ɗorewar cigaba na 2026, wanda za a gudanar a farkon Janairun sabuwar shekara.

Kakakin na Tinubu ya ce taron na tsawon mako ɗaya an saba yin sa ne domin haɗa shugabannin gwamnati, ƴan kasuwa da kuma al’umma don tattaunawa a taron.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!