Connect with us

Labarai

Tinubu ya taya Soludo murna bisa sake lashe zaɓen gwamnan Anambra

Published

on

Shugaban kasa Bola Tinubu ya taya murna ga gwamnan jihar Anambra, Charles Soludo bisa samun nasarar sake lashe zaɓen gwamnan jihar da aka gudanar ranar Asabar, inda ya yaba wa mutanen jihar bisa gudanar da zaɓen cikin lumana.

A cikin wata sanarwa da ya wallafa a kafofin sada zumuna Tinubu ya kuma yaba wa ƙoƙarin da ya ce, hukumar zaɓen Najeriya INEC ta yi.

Shugaban ya ce ya ziyarci jihar a watan Mayun da ya gabata domin ƙaddamar da wasu ayyuka da gwamnan ya yi, waɗanda ya bayyana da ayyuka masu muhimmanci da nagarta

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya kuma yaba wa Soludo bisa yadda yake gudanar a mulki mai kyau domin ciyar da jihar Anambra gaba. Sannan ya yi kira gare shi da ya janyo abokan hamayyarsa kusa domin haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen ciyar da jihar gaba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!