Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Tokyo 2020: Rukunin farko na tawagar Najeriya zai tashi zuwa Tokyo

Published

on

Rukunin farko na tawagar ‘yan wasan da za su wakilci Najeriya a gasar Olympics ta 2020 da za a gudanar a Tokyo, za su tashi daga Najeriya zuwa kasar Japan.

An bayyana hakan ne a wata sanarwa da jami’in yada labaran ma’aikatar wasanni ya rabawa manema labarai.

Tawagar ‘yan wasan za su tashi daga Najeriya ta jirgin Ethiopian Airline a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe dake Abuja.

Najeriya dai za ta fafata a wasanni tara wadanda za a fara daga 23 ga watan Yuli zuwa 8 ga Agusta, yayin da guragu za su fafata a wasanni hudu daga ranar 24 ga watan Agusta zuwa 5 ga watan Satumbar 2021.

A halin yanzu, hukumar wasannin guje-guje da tsalle-tsalle ta duniya (WA) ta tabbatar da cewa Najeriya za fafata wasanni 13 ne a gasar da za a gudanar a birnin Tokyo dake kasar Japan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!