Connect with us

Labarai

Trump na shirin kaddamar da hare-hare a Iran

Published

on

Shugaba Trump ya ce lokaci na ƙurewa gwamnati Iran na hawa teburin tattaunawa. A cewar sa idan gwamnatin ta gaza hakan, ya yi gargaɗin cewa hari na gaba da zai kai mata, zai fi wanda da aka kai cibiyoyin nukiliyarta a watan Yunin bara muni.

Mista Trump ya ce wasu manyan jiragen ruwan yaƙi na tunkarar Iran, inda ya ce a shirye suke su kammala aikinsu cikin gaggawa, kamar yadda dakarun Amurka suka kai hari Venezuela.

Tun da farko dai ministan harkokin wajen Iran ya ce bai yi wata tattaunawa da Amurka ba a kwanakin baya bayan nan, kuma bai buƙaci a yi wata tattaunawa ba.

Sai dai Abbas Araqchi ya ce masu shiga tsakani da dama, waɗanda bai bayyana sunayensu ba, na neman shawarwari da kuma ganawa a Tehran.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!