Labarai
Trump na shirin kaddamar da hare-hare a Iran

Shugaba Trump ya ce lokaci na ƙurewa gwamnati Iran na hawa teburin tattaunawa. A cewar sa idan gwamnatin ta gaza hakan, ya yi gargaɗin cewa hari na gaba da zai kai mata, zai fi wanda da aka kai cibiyoyin nukiliyarta a watan Yunin bara muni.
Mista Trump ya ce wasu manyan jiragen ruwan yaƙi na tunkarar Iran, inda ya ce a shirye suke su kammala aikinsu cikin gaggawa, kamar yadda dakarun Amurka suka kai hari Venezuela.
Tun da farko dai ministan harkokin wajen Iran ya ce bai yi wata tattaunawa da Amurka ba a kwanakin baya bayan nan, kuma bai buƙaci a yi wata tattaunawa ba.
Sai dai Abbas Araqchi ya ce masu shiga tsakani da dama, waɗanda bai bayyana sunayensu ba, na neman shawarwari da kuma ganawa a Tehran.
You must be logged in to post a comment Login