Connect with us

Labarai

Tsaro: Ana ci gaba da yin sulhu da ‘yan bindiga a Katsina

Published

on

Ƙananan hukumomin Malumfashi da Funtua da Bakori sun bi sahun wasu takwarorinsu da suka yi sulhu da ƴanbindigar a jihar da ke fama da matsalar tsaro.

Jihar Katsina na daga cikin jihohin arewa maso yammacin Najeriya da ke fama da matsalar ƴanbindiga masu kai hare-hare a ƙauyuka da garuruwan jihar da kashe mutane da sace wasu domin neman kuɗin fansa.

An gudanar da zaman sulhun ne a garin Kakumi da ke yankin ƙaramar hukumar Bakori, kamar yadda Jaridar Daily Trust ta bayyana.

Taron sulhun ya samu halartar shugabannin alumomin yankunan da wakilan ƴanbindigar.

A baya-bayan nan ana ta samun ƙaruwar hare hare a ƙananan hukumomin Katsina inda a ka rungumar sulhu a wani mataki na magance matsalar tsaron jihar.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!