Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Tsaro: Gwamnonin yankin Kudu maso gabashin Najeriya sun kafa kungiyar sintiri

Published

on

Gwamnonin yankin Kudu maso gabashin kasar nan sun bi sahun takwarorinsu na Kudu maso yammaci wajen kafa kungiyar sintiri da za ta kare yankin daga ayyukan bata-gari.

Shugaban kungiyar gwamnonin yankin kuma gwamnan Jihar Ebonyi Dave Umahi ne ya karanta takardar bayan taro ga manema labarai a birnin Owerri na jihar Imo.

“Mun bijiro da tsarin ne domin kyautata harkokin tsaro a yankin namu,” inji Dave Umahi.

Umahi ya ce kungiyarsu ta yi allawadai da harin da wasu bata-gari suka kai a ofishin ‘yan sanda da gidan gyaran hali a Jihar ta Imo, inda suka hallaka wasu mutane ciki har da jami’an tsaro sannan suka saki daurarrun gidan.

A baya dai gwamnonin Kudu maso yammacin kasar nan sun sanyawa kungiyar sintirin ta yankinsu sunan Amotekun, yayin da ita kuwa ta kudu maso gabashi ta sanyawa ta ta sunan Ebube Agu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!