Connect with us

Labarai

Tsohon mataimakin shugaban kasa Namadi Sambo, ya musanta yin sauyin sheka

Published

on

Tsohon mataimakin shugaban kasa Namadi Sambo, ya yi watsi da rahoton ficewar sa daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

Namadi Sambo, a cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yada labarai, Umar Sani, ya fitar, ya bayyana rahoton sauya sheka a matsayin kage ne da nufin bata suna.

Sanarwar ta kara da cewa, hoton tsohon mataimakin shugaban kasar Namadi Sambo da gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, da ake yadawa a kafafen yada labarai, ya yi amfani da shi a labarin sauya shekar, tsohon hoto ne.

Sanarwar ta kara tabbatar da cewa tsohon mataimakin shugaban kasan jigo ne kuma jagora a jam’iyyar PDP da ba shi da niyyar shiga wata jam’iyyar siyasa bayan wadda ya ke ciki.

Idan dai za a iya tunawa a ranar Larabar da ta gabata ne aka samu labarin ficewar Sani Sidi, wanda ke zama na hannun daman tsohon mataimakin shugaban kasar zuwa jam’iyyar APC tare da magoya bayansa a Kaduna.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!