Connect with us

Labarai

Turkiyya ta bayyana shirinta na taimakawa Najeriya

Published

on

Shugaban ƙasar Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan ya ce ƙasarsa a shriye take ta taimakawa Najeriya wajen yaki da ta’addanci, yayin da ƙasar ke neman taimakon ƙasashen duniya don magance matsalolin tsaro da suka haɗa da ƙaruwar satar mutane a baya-bayan nan.

 

Erdogan ya yi wannan bayani ne a taron manema labarai tare da Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, a birnin Ankara, inda ya ce “Turkiyya a shirye take ta bayar da ƙwarewar da take da ita a fannin tsaro da yaki da ta’addanci domin taimakawa Najeriya.

 

Tinubu ya bayyana cewa taimakon zai haɗa da “horon soji da na tattara bayanan sirri, da kuma ayyukan yaƙi da ta’addanci.

 

Shugabannin biyu sun tattauna kan bunƙasa haɗin gwiwar tattalin arziki, inda shugaba Erdogan ya ce Turkiyya za ta ƙulla kasuwancin dala biliyan 5 da Najeriya.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!