Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Dan sanda yayi sanadiyar ajalin wani dan kasuwa

Published

on

Wani dan kasuwa ya gamu da ajalinsa sakamakon harbin bindiga da wani dan sanda yayi masa.

Dan sandan  dai yana gadi ne a wani Banki  yayin da ya hango wannan mai mota ya buge wani mutum kuma wasu ‘yan sanda dake aiki a bakin titi suka  bukaci shi daya bude motarsa a saka wanda yaji raunin amma kuma yaki bayan da aka yi zargin cewar yana son ya tsere.

Amma sai yaki bin umarnin su hakan ya sanya dan sanda  dake zaune yana aikin gadi ya ja kunamar bindigarsa ya harbi wannan matukin motar kuma nan take ya rasu.

Rundunar ‘yan sanda ta Kano ta yi holin masu yin garkuwa da mutane

Kano: Lauyoyi sun yi barazanar gurfanar da kwamishinan ‘yan sanda

Jihar Kano ta sami sabon kwamishinan ‘yan sanda

Hakan tasa abokin tafiyar direban ya kasa magana saboda dimaucewa da yayi ganin abinda yafaru da wanda suke tare.

Tuni dai tawagar ‘yan sanda suka halacci gurin da abin yafaru  karkashin jagorancin babban mukaddashin kwamishinan’ yan sanda na Kano mai lura da ayyukan yau da kullum DSP Balarabe sule.

Kakakin rundunar ‘yan sanda ta jihar DSP Abdullahi Haruna ya ce rundunar na tattara bayanai kafin gurfanar da wanda ake zargi a kotu

 

 

 

 

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!