Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Wani kwararren mai bincike ya sha alwashin kwato kudaden gwamnati da aka wawure

Published

on

Wani kwararren mai bincike mai zaman kansa da kwamitin shugaban kasa da ke kwato dukiyar kasar nan da aka sace ya dauko hayarsa, Evangelist Victor Uwajeh, ya sha alwashin shiga lunguna da sakuna na kasar nan domin tabbatar da cewa dukkannin kudade da kadarorin gwamnati da aka wawure sun dawo gareta.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun sa wanda aka rabawa manema labarai jiya a Abuja.

Ta cikin sanarwar dai an kuma ruwaito Evangelist Victor Uwajeh na neman hadin kan ‘yan majalisun dokokin tarayya da bangaren shari’a domin samun nasarar shirin.

Evangelist Victor Uwajeh wanda fitaccen mai bincikar kadarorin da aka boye ne na kasa da kasa, ya ce, ya karbi aikin ne domin tallafawa kokarin da shugaba Muhammadu Buhari ke yi wajen kawadda masu ci da gumin al’ummar kasar nan.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!