Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Wasan hamayya: Manchester City ta lallasa Manchester United a gasar Firimiya

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester City ta casa Manchester United a gasar Firimiya ta kasar Ingila da ci 4-1.

Filin wasa na Etihad ne ya karbi bakuncin wasan da ya gudana a ranar Lahadi 06 ga Maris din 2022.

Manchester United da Manchester City dai na hamayya da juna, wanda hakan ya sa fafatawar ta dauki hankalin magoya bayan kungiyoyi biyun.

Dan wasa Kevin De Bruyne ne ya zura kwallaye biyu a minti na (4′) da (27′)

Kana shima dan wasan kasar Algeria Riyard Mahrez ya zura kwallaye biyu a mintuna na (67′) da (90′)

Sai dai dan wasan Manchester United da kasar Ingila Jadon Sancho ya zura kwallo daya a minti na (21′) da jumulla kungiyarsa tayi rashin nasara da ci 4-1.

Kawo yanzu Manchester City na matakin farko da maki 69 a wasanni 28 da ta buga.

Yayinda kungiyar kwallon kafa ta Manchester United take a mataki na biyar da maki 47.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!