Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Wata kungiya a Fagge ta mika wasikar kiranye ga shugaban majalisar dokoki

Published

on

Wata kungiya mai rajin ci gaban al’ummar Fagge mai suna Fagge Civil Society ta mika da wasika ga hukumar zabe ta kasa INEC wanda a ciki ta bukaci yin kiranye ga shugaban majalisar dokokin jihar Kano Yusuf Abdullahi Ata.

Wasikar wanda aka mikashi a jiya Talata ga shugaban hukumar zabe ta kasa Farfesa Mahmud Yakubu a shalkwatar hukumar ta INEC da ke Abuja, ta bayyana cewa yin kiranyen ya yi daidai da sashe na 110 na kundin tsarin mulkin kasar nan.

Sakataren kungiyar Amar Sanusi Laure ne ya sanya hannu kan wasikar a madadin kungiyar.

Wasikar kungiyar ta kuma kunshi sanya hannun wasu al’ummar mazabar Fagge wadanda kungiyar ta ce suna daga cikin jama’ar mazabar da suka kada kuri’a ga dan majalisar wadanda kuma a yanzu suka yanke kauna da jagorancin da ya ke yi musu.

A wata wasikar kuma kungiyar ta zargi sakataren mulki na hukumar zabe ta kasa shiyyar Kano da kin bata hadin kai wajen mika musu wasu muhimman bayanai da kungiyar za ta yi amfani da su wajen gudanar da kiranyen.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!